Laifuka

Jami'an Tsaro Sun Kama Wanda Ya Kashe Kwamandan 'yansanda A Yankin Dutsinma

Jami'an tsaro sun kama wanda ya kashe Kwamandan 'yansanda a yankin Dutsinma 'Yan sandan Katsina sun kama ɗaya daga cikin 'yanta'addan da a kwanakin baya suka kashe kwamandan yankunan ƙaramar hukumar Dutsinma, ACP Aminu Umar. Rundunar ‘yansanda a jihar Katsina ta ce ta kama wani ɗanbindiga mai shekaru 30, wanda ake zargin yana da hannu wajen kashe Kwamandan yankin Dutsinma, ACP Aminu Umar. Kamar yadda Katsina Post ta samu, jami'in hulɗa da jama'a na rundunar 'yansandan jihar Katsina ASP Abubakar Sadiq Aliyu shi ne ya bayyana haka a lokacin taron Manema Labarai a ranar Alhamis 14 ga watan Satumba 2023. Yace rundunar ‘yansandan da ke sintiri ta samu galaba a kan ‘yanbindigar ne a wani artabu da suka yi da ta kai ga rasa ransa da na wani jami’i wanda aka fi sani da Sabon Jini, an kama shi ne a ranar 30 ga watan Agusta. Wanda ake zargin ya fito ne daga Ƙauyen Tsaskiya da ke ƙaramar hukumar Safana a jihar Katsina. A cewar rundunar 'yansandan, wanda ake zargi ya kasance cikin jerin sunayen da rundunar 'yansandan ta ke nema ruwa a jallo bisa wasu laifuffuka, kamar satar mutane. Satar shanu da sauran munanan laifuka. ASP Abubakar Sadiq Aliyu yace wanda ake zargin an kama shi ne a lokacin da aka kama shi gameda da laifin yin garkuwa da wani Hussaini Nabara da ke Ƙauyen Kagara a ƙaramar hukumar Dutsinma, inda a nan ne ya tabbatar da faruwar lamarin a yayin zurfafa bincike aka gano shi danƙungiyar wani Abubakar ne mai suna Jankare, wanda fitaccen shugaban ‘yanfashi ne a yankin Dutsinma Tunda farko wanda ake zargin ya amsa laifin haɗa baki da wasu miyagun ‘yanbindiga domin yi wa marigayi ACP Umar kwanton ɓauna a yayin da rundunar ta kama mutum 35 a ranar 2 ga watan Satumba, a yayin da ake gudanar da bincike wanda ake zargin ya amsa laifin da ake zargin sa da shi. Idan ma su bibiyar labarai ba su manta ba, a ranar 5 ga watan Yuli ne ‘yanbindiga suka yi wa marigayi ACP Umar kwanton ɓauna suka kashe shi, yayin da yake jagorantar tawagar sintiri a aikin da suka saba yi na fatattakar ‘yanta’adda a yankin Dutsinma.

An Kama Wani Mutum Da Buhun Alburusai Zai Kai Ma Yan Bindiga A Katsina

An kama wani mutum da buhun alburusai zai kai ma yan bindiga a Katsina Jami'an tsaro a jihar Katsina sun daƙile yunƙurin wani matashi bata-gari mai suna Ibrahim Abdullahi, na safarar alburusai zuwa ga yan bindiga a jihar Katsina. Kamar yadda Katsina Post ta samu, matashin wanda ya ce shekarun sa 35 a duniya, yana kokarin shigar da alburusan ne zuwa daji wurin yan bindiga daga kauyen su na Sabon Garin Dunburawa, na karamar hukumar Batsari a Jihar Katsina. Da jami'an tsaron ke tuhumar sa, Ibrahim Abdullahi ya ce zai kai wa wani dan bindiga ne mai suna Yusuf alburusan can yammacin garin na Dumburawa bakin lamba. Haka zalika bata-garin ya kuma bayyana nadamar sa sannan ya nuna sha'awar sa ta bayar da gudummuwa wajen kamo ɗan ta'addan.

Cikin Shekaru 8 An Sace Ma'aikatan Lafiya 83, An Kashe 16 A Katsina

Kungiyar ma’aikatan lafiya ta Najeriya MHWUN reshen jihar Katsina ta bayyana cewa ƴan ta’adda sun sace ma’aikatan lafiya 83 tsakanin shekarar 2015 zuwa 2023 a fadin jihar. Majiyar Jaridar Katsina Post ta Thisday ta ruwaito cewa Shugaban kungiyar na jiha, Mannir Mohammed Suleiman ne ya bayyana haka a daren Laraba a liyafar cin abinci na karrama Dr. Shamsudeen Yahaya bisa sake nada shi a matsayin babban sakataren hukumar lafiya a matakin farko ta jihar. Ya bayyana cewa daga cikin mutane 83 da aka sace, an sako 65 bayan an biya su kudin fansa, yayin da 16 ‘yan ta’addan suka kashe a garuruwa daban-daban a fadin jihar. Shugaban na MHWUN ya kara da cewa daya daga cikin waɗanda abin ya rutsa da su ya tsere daga hannun wadanda aka yi garkuwa da su da harbin bindiga, yayin da wani ma’aikacin lafiya kuma ba a ga inda yake ba tun shekaru hudu da suka gabata. Ya ce: “Muna godiya ga gwamnatin jihar wajen samar da rijistar ma’aikata a dukkan ma’aikatu da hukumomi na gwamnati. Amma muna kuma rokon gwamnati da ta sake duba rijistar musamman a kananan hukumomin da ke da babban kalubale na rashin tsaro. “Kamar yadda nake magana da ku yanzu, an yi garkuwa da kusan ma’aikatan lafiya 83 a fadin jihar. Daga cikin adadin, an saki 65 bayan an biya kudin fansa yayin da aka kashe mutum 16. “Daga cikin adadin, mutum ɗaya ya tsere da harbin bindiga sannan kuma ba a ga wani mutum guda ba a cikin shekaru hudu da suka gabata. Muna ƙara yin kira ga gwamnati da ta magance matsalolin tsaro a jihar.” Sai dai ya koka kan karancin ma’aikata a fannin kiwon lafiya a jihar, inda ya kara da cewa kashi 50 zuwa 60 na ma’aikatan lafiya a hukumar kula da asibitoci da kuma hukumar kula da lafiya a matakin farko na jihar ma'aikatan wucin gadi ne wasu kuma masu aikin sa kai ne. Ya kuma bayar da shawarar aiwatar da daftarin inganta kiwon lafiya matakin farko da daraktocin ruwa, tsaftar muhalli da tsafta (WATSAN) daga mataki na 15 zuwa 16 a jihar. Haka kuma Suleiman ya yi kira ga gwamnatin jihar da ta duba yiwuwar shigar da ma’aikatan inganta jin dadin jama’a wajen yaki da cututtuka da kuma magance cututtuka a wani bangare na ayyukansu a jihar.

Cikin Shekaru 8, Ƴan Ta’adda Sun Sace Ma’aikatan Lafiya 83, Sun Hallaka 16 A Katsina

Cikin Shekaru 8, Ƴan Ta’adda Sun Sace Ma’aikatan Lafiya 83, Sun Hallaka 16 A Katsina Kungiyar ma’aikatan lafiya ta Najeriya MHWUN reshen jihar Katsina ta bayyana cewa ƴan ta’adda sun sace ma’aikatan lafiya 83 tsakanin shekarar 2015 zuwa 2023 a fadin jihar. Majiyar Jaridar Katsina Post ta Thisday ta ruwaito cewa Shugaban kungiyar na jiha, Mannir Mohammed Suleiman ne ya bayyana haka a daren Laraba a liyafar cin abinci na karrama Dr. Shamsudeen Yahaya bisa sake nada shi a matsayin babban sakataren hukumar lafiya a matakin farko ta jihar. Ya bayyana cewa daga cikin mutane 83 da aka sace, an sako 65 bayan an biya su kudin fansa, yayin da 16 ‘yan ta’addan suka kashe a garuruwa daban-daban a fadin jihar. Shugaban na MHWUN ya kara da cewa daya daga cikin waɗanda abin ya rutsa da su ya tsere daga hannun wadanda aka yi garkuwa da su da harbin bindiga, yayin da wani ma’aikacin lafiya kuma ba a ga inda yake ba tun shekaru hudu da suka gabata. Ya ce: “Muna godiya ga gwamnatin jihar wajen samar da rijistar ma’aikata a dukkan ma’aikatu da hukumomi na gwamnati. Amma muna kuma rokon gwamnati da ta sake duba rijistar musamman a kananan hukumomin da ke da babban kalubale na rashin tsaro. “Kamar yadda nake magana da ku yanzu, an yi garkuwa da kusan ma’aikatan lafiya 83 a fadin jihar. Daga cikin adadin, an saki 65 bayan an biya kudin fansa yayin da aka kashe mutum 16. “Daga cikin adadin, mutum ɗaya ya tsere da harbin bindiga sannan kuma ba a ga wani mutum guda ba a cikin shekaru hudu da suka gabata. Muna ƙara yin kira ga gwamnati da ta magance matsalolin tsaro a jihar.” Sai dai ya koka kan karancin ma’aikata a fannin kiwon lafiya a jihar, inda ya kara da cewa kashi 50 zuwa 60 na ma’aikatan lafiya a hukumar kula da asibitoci da kuma hukumar kula da lafiya a matakin farko na jihar ma'aikatan wucin gadi ne wasu kuma masu aikin sa kai ne. Ya kuma bayar da shawarar aiwatar da daftarin inganta kiwon lafiya matakin farko da daraktocin ruwa, tsaftar muhalli da tsafta (WATSAN) daga mataki na 15 zuwa 16 a jihar. Haka kuma Suleiman ya yi kira ga gwamnatin jihar da ta duba yiwuwar shigar da ma’aikatan inganta jin dadin jama’a wajen yaki da cututtuka da kuma magance cututtuka a wani bangare na ayyukansu a jihar.

‘Yansanda Sun Kama Mutane 10 Da N144,000 Na Kuɗin Jabu A Katsina

‘Yansanda sun kama mutane 10 da N144,000 na kuɗin jabu a Katsina Rundunar ‘yan sandan jihar Katsina, ta kama wasu mutane 10 da ake zargi da yin damfara da buga takardun kuɗi na bogi har N144,000. Kakakin rundunar ‘yan sandan, ASP Aliyu Abubakar-Sadiq ne ya bayyana hakan yayin da yake holen su a Katsina ranar Juma’a. A cewarsa, ‘yan sanda sun kama wadanda ake zargin ne a ranar 28 ga watan Agusta, a unguwar Bakin Kasuwa da ke Kankia, biyo bayan wani bayanan sirri da suka samu. Abubakar-Sadiq ya ƙara da cewa, a yayin gudanar da bincike, waɗanda ake zargin sun amsa laifin da suka aikata, inda ya ce nan ba da jimawa ba za a gurfanar da su a gaban kotu. Daya daga cikin wadanda ake zargin, Bello Abubakar mai shekaru 58, ya ce ya sayi sinadarin Mercury daga Kebbi kan Naira 300,000 da ake amfani dashi wajen buga kudin jabun. Katsina Post ta riwaito cewa rundunar ‘yan sandan ta kuma sanar da cafke wasu mutane hudu da ake zargin masu garkuwa da mutane ne da kuma mai basu labarai.

'Yanbindiga Sun Buɗe Wani Sabon Shafi A ƙaramar Hukumar Danmusa

'Yanbindiga sun buɗe wani sabon shafi a ƙaramar hukumar Danmusa 'Yanbindiga sun addabi ƙaramar hukumar Danmusa tin lokacin da Sojoji suka fara kamensu a kasuwar garin. Majiyar Katsina Post ta samu cewa ko a ranar Alhamis 31 ga watan Agusta na 2023, sun ƙara kai hari a garin Danmusa a unguwar Tukane inda suka shiga gidan wani Dan-asibi mai wanki da guga suka yi awon gaba da matarsa. Tun da farko, yawaitar hare-haren na zuwa ne sati biyu da suka wuce bayan da jami'an tsaron sojojin Najeriya suka shigo cikin kasuwar ta Danmusa sukai ta kama 'yanbindigar. Haka zalika, ko a jiya Alhamis 31 08 2023 sun kai hari a garin Maidabino dake cikin ƙaramar hukumar Danmusa inda suka yi ajalin kashe wani matashi mai suna Tukur Abdulmumini mai shekara 33. Harin da 'yanbindigar suka kai a Maidabino ya ƙara ba kowa mamaki ganin yadda kilomita ɗaya da cikin garin Maidabino akwai jami'an tsaron sojojin Najeriya jifge a sakandaren jika ka dawo ta garin. Majiyar ta ce ko a sati biyu da suka wuce sun kai harin a Maidabino inda suka yi ajalin wani mutum tare da yin garkuwa da matar shi da kore mashi Dabbobinsa. Al'ummar yankunan na cigaba ta tofa albarkacin bakin su na gani cewa Gwamnati ta dubi Girman Allah ta agaza ma su domin ƙaramar hukumar Danmusa tana fama da hare-haren 'Yanbindiga inda yanzu babu wani ƙauyen da ba su ɗai-ɗaita shi ba.

'Yanbindiga Sunyi Garkuwa Da Mata Uku 'Yan Gida Ɗaya A Garin Danmusa

'Yanbindiga Sunyi Garkuwa Da Mata Uku 'Yan Gida Ɗaya A Garin Danmusa Wasu 'Yanbindiya ɗauke da manyan makamai sun shigo cikin garin Danmusa inda suka yi garkuwa da wasu 'Yan Mata 2 da mahaifiyar su ta 3 a cikin ƙaramar hukumar Danmusa. Majiyar da Katsina Post ta samu gameda faruwar harin, lamarin ya faru ne a cikin wata Unguwa da ake ma laƙabi da Mangwarora dake garin Danmusa. Majiya mai tushe tace lamarin ya faru ne a ranar Alhamis 31 ga watan Agusta 2023, da misalin karfe 2:00 na dare inda suka afkama gidan wani mutum mai suna Malam Zubairu Zakki inda sukayi awon gaba da matar shi da 'ya'yan shi Biyu 'yan mata. A halin yanzu mutanen yankunan na cigaba da damuwa ganin yadda matsalar tsaro ke ƙara ruruwa kamar wutar daji duk da mahukuntar yankin na iya bakin ƙokarin su. An ce ko a ranar talatar da ta gabata sai da 'yan bindiyar suka shiga Unguwar Teloli a ƙaramar hukumar inda suka harbi Mutum Biyu, inda ya zuwa yanzu suna Kwance a Asibitin ƙaramar hukumar Danmusa.