
Masarautar Katsina ta tsige Alhaji Abubakar Abdullahi Amadou daga sarautar shi ta Sarkin Kurayen Katsina, Hakimin Kuraye.
Wannan na ƙunshe a cikin wata sanarwar da sakataren masarautar Katsina, Sarkin Yaƙin Katsina, Alhaji Bello Mamman Ifo ya sanya ma hannu.
Sanarwar ta bayyana cewa Gwamnatin jihar Katsina ce ta bada umarnin tsige hakimin daga sarautar shi.
Ga wasiƙar da masarautar ta aikewa hakimin:
YI MAKA RITAYA DAGA SARAUTAR SARKIN KURAYEN KATSINA, HAKIMIN KURAYE:
Bisa
Don haka, Masarautar Katsina ta yi maka Ritaya daga Sarautar Sarkin
Kurayen Katsina daga Yau Litinin 18/9/2023.
Da fatan Allah Ya bamu lafiya da zama lafiya amin.
Comments