• Follow Us:  

Latest News

Gwamna Raɗɗa Ya Sauke Shugaban Hukumar Tattara Haraji Ta Jihar Katsina

Gwamna Raɗɗa ya sauke shugaban hukumar tattara haraji ta jihar Katsina Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umar Radda ya cire sabon shugaban hukumar tattara haraji ta jihar. Wannan da na kunshe ne a cikin wata takardar da aka aikawa shugaban hukumar ranar Litinin, 19 ga watan Satumba, 2023 daga ofishin Sakataren Gwamnatin jihar. A cikin takardar, an bayyana cewa an cire shugaban hukumar ne biyo bayan janye tantancewar da majalisar dokokin jihar Katsina ta yi ma shi a kwanan baya. Mai karatu zai iya tuna cewa a kwanan baya ne Gwamnan ya tura sunan Prof Sani Mashi majalisar dokokin jihar Katsina domin su tantance shi a matsayin shugaban hukumar tattara haraji ta jihar. Bayan sun tantance shi, daga baya kuma sai majalisar ta ce ta gano wasu kurakurai a tattare da shi wanda kuma suka janye tantancewar da suka yi masa.

PTAD Sensitize Pensioners In Katsina On Newly Introduced “I Am Alive" Service

“I Am Alive" online confirmation of PTAD pensioners nationwide PTAD sensitize pensioners on newly introduced “I Am Alive" service The Pension Transitional Arrangement Directorate (PTAD) carried out a sensitization exercise of its ongoing “I AM AlIVE" online confirmation of pensioners under the Defined Benefits Scheme to retired workers in security sector, in an effort to identify pensioners that are alive for their prompt payment. The sensitization program took place on Monday, September 19, 2023, at the premises of the police compound at GRA in Katsina Metropolis. Speaking at the event, the leader of the exercise, Hajiya Bilkisu Rimi, said that the "I am Alive" program, which is being carried out, aims to determine the pensioners of the federal government who are alive by verifying themselves using the online program launched by the Directorate. Apart from that, she noted that the scheme was introduced looking at the current situation in the country to ease the untold hardship experienced by the retired workers in trying to get verified. She noted that the new introduced program would enable the pensioners to verify themselves using smart phone or computer laptop. According to her, in order to ensure prompt payment of pension to retired workers, it launched the scheme for the retired workers to verify themselves every six months. In his remark, Dr. Abubakar Dan Musa from the National Health Insurance Scheme (NHIS) said the cardinal objectives of the agency is to ensure the provision of health care delivery at subsidized rate. He noted that the NHIS would use the information gotten from PTAD to include retired workers in to the scheme, while calling on people to register with the agency to benefits with the agency. In another development, the leaders of the Directorate has paid a courtesy visit to the Emir of Katsina Dr. Abdulmuminu Kabir Usman and other traditional monarchs to continue to sensitize the pensioners on how to make good use of the opportunity introduced by PTAD. In a remark the Emir of Katsina, Alhaji Abdulmuminu Kabir Usman, expressed his happiness over the introduction of the new scheme to ease the difficulty experience by the pensioners. The royal Father noted that the online confirmation of pensioners will ease the difficulties experienced by the retired workers for their payments. The Emir, added it will significantly impact on the lives of pensioners, who spent years contributing to the development of the nation. He called on them to live above board in discharging their assigned their responsibilities.

Majalisa Ta Buƙaci A Rufe Wurin Sharholiya Na Luna Otel Din-din-din Dake Garin Katsina

Majalisa ta buƙaci a rufe wurin sharholiya na Luna Otel din-din-din dake garin Katsina Majalisar dokokin jihar Katsina ta nemi Gwamnatin jihar Katsina ta ɗauki matakin gaggawa na rufe shahararren otel din nan Luna dake a cikin garin Katsina. Ɗanmajalisa mai wakiltar ƙaramar hukumar Katsina, Hon. Ali Abu Albaba shi ne ya gabatar da ƙudirin wanda ya samu goyon bayan illahirin ‘yanmajalisar dokokin. Kamar yadda Katsina Post ta rawaito, yayin gabatar da ƙudirin, ɗanmajalisar ya koka da gudummuwar da otel ɗin ke badawa wajen ɓata tarbiyar yara Mata musamman ƙananan Yara a Katsina. Hon. Albaba ya bayyana cewa Luna ta zama dandalin dake tara ‘yanmata ƙanana, da ake shan barasa da kuma mafaka ga miyagu masu aikata laifuka daban-daban. Haka kuma yace akwai sauran wuraren sharholiya dake a cikin garin Katsina waɗanda ya kamata Gwamnati ta rufe bisa ayyukan assha da akeyi da suka saɓa dokokin jihar. Yayi tuni ga zauren a kan dokar da ‘yanmajalisar suka yi na hana sha da sai da giya da wasu manyan laifuka a jihar wanda a cewar shi, Otel din Luna na ɗaya daga cikin wuraren da ake aiwatar da hakan. Hon. Albaba ya kara da cewa mafi yawancin masu buɗe wuraren ba ‘yan jiha ba ne kuma suna taimakawa wajen gurɓata tarbiyar ‘yan jihar Katsina. Ya roki zauren majalisar ya amince a tura ma ɓangaren zartarwa buƙatun majalisar domin a ɗauki matakin rufe otel din baki ɗaya.

Yadda Jerin Farashin Abinci Yake Yau Laraba A Wasu Kasuwannin Jihar Katsina.

Yadda jerin farashin Abinci yake yau Laraba a wasu Kasuwannin jihar Katsina. Kasuwar garin Ingawa,ga yadda farashin sa yake kamar haka; 1- Buhun Masara - 48,000 sabuwa - 39,000 2- Buhun Dawa - 35,000 Mori - 39,000 Fara - 34,000 3- Buhun Gero - 39,000 4- Buhun Maiwa - 38,000 5- Buhun Shinkafa - 76,000 shenshera - 25,000 6- Buhun Gyada - 59,500 Mai bawo - 25,000 7- Buhun Wake kana - 32,000 manya - 44,000 sabo - 31,000 8- Buhun Waken Suya - 33,000 9- Buhun Alabo - 38,000 10- Buhun Tarugu - 28,000 11- Buhun Dankali - 9,000 Kasuwar garin Danmusa, ga yadda farashin sa yake kamar haka; 1- Buhun Masara - 42,000 2- Buhun Dawa - 52,000 3- Buhun Gero - 37,000 4- Buhun Dauro - 49,000 4- Buhun Shinkafa - 68,000 Shanshera - 29,000 5- Buhun Gyada - 74,000 Mai bawo - 26,000 6- Buhun Waken suya - 38,000 7- Buhun Wake - 44,000 8- Buhun Aya - 43,000 kanana - 38,000 9- Buhun Alabo - 27,000 10- Buhun Tattasai - 23,000 11- Kwandon Tumatur - 5,600 12- Buhun Tarugu - 8,800 13- Buhun Dabino - 85,000 14- Buhun Barkono - 22,000 15- Buhun Dankali - 14,000 16- Buhun Albasa - 22,000 17- Buhun Tsamiya - 16,000 Kasuwar garin kankara, ga yadda farashin sa yake kamar haka; 1- Buhun Masara - 45,000 sabuwa - 32,000 2- Buhun Dawa - 42,000 3- Buhun Dauro - 42,000 4- Buhun Gyada - 75,000 5- Buhun Wake - 50,000 Sabo - 40,000 6- Buhun Waken suya - 32,000 7- Buhun Garin Kwaki - 28,000 8- Buhun Alabo - 42,000 9- Buhun Albasa - 20,000 10- Buhun Barkono - 20,000 Kasuwar garin Ajiwa a Karamar Hukumar Batagarawa, ga yadda farashin sa yake kamar haka; 1- Buhun masara - 37,000 2- Buhun Dawa - 45,000 3- Buhun Gero - 39,000 4- Buhun Gyada - 71,000 5- Buhun wake - 50,000 6- Buhun waken suya - 42,000 7- Buhun Alabo - 35,000 8- Buhun Albasa - 19,000 9- Buhun Dankali - 18,000 10- Buhun Barkono - 37,000 11- Buhun Garin Kwaki - 25,000 Kasuwar garin Bakori,ga yadda farashin sa yake kamar haka; 1- Buhun masara - sabuwa - 30,000 2- Buhun Dawa - 41,000 3- Buhun Gero - 54,000 sabo - 30,000 4- Buhun Dauro - 60,000 5- Buhun Alabo - 40,000 6- Buhun Gyada tsaba - 75,000 mai bawo - 23,000 7- Buhun Shinkafa tsaba - 70,000 shanshera - 28,000 8- Buhun Wake - 36,000 sabo - 46,000 9- Buhun waken suya - 38,000 10- Buhun Barkono - 37,000 11- Buhun Dankali - 16,000 12- Kwandon Tumatur - 2,000 kauda - 15,000 13- Buhun Tarugu - 21,000 14- Buhun Albasa - 26,000 lawashi - 1,800 Kasuwar garin Mashi,ga yadda farashin sa yake kamar haka; 1- Buhun masara - 44,000 sabuwa - 36,000 2- Buhun Dawa - 40,000 3- Buhun Gero - 34,000 4- Buhun Kalwa - 40,000 5- Buhun Sobo - 35,000 6- Buhun wake - 44,000 7- Buhun waken suya - 43,000 sabo - 36,000 8- Buhun tattasai - 40,000 9- Buhun Tumatur kauda - 19,000 10- Buhun Aya kanana - 38,000 manya - 47,000 11 Buhun Barkono - 18,500 12- Buhun Dankali - 15,000 13- Buhun Lalle - 13,000 Kasuwar garin funtua, ga yadda farashin sa yake kamar haka; 1- Buhun Masara - 52,000 sabuwa - 32,000 2- Buhun Dawa - 44,000 3- Buhun Gero - 34,000 4- Buhun Dauro - 5- Buhun Shinkafa - 76,000 samfarera - 25,000 6- Buhun Wake - 48,500 7- Buhun Waken Suya - 38,000 tsoho - 45,000 8- Buhun Tattasai - 9- Kwandon Tumatur- 2,500 10- Buhun Tarugu - 9,000 11- Buhun citta - 44,500 12- Buhun taki Yuri - 20,700 Daga Aysha Abubakar Danmusa.

Gwamnatin Jihar Katsina Za Ta ƙirƙiro Wutar Lantarki A Wasu Asibitocin Jihar

Gwamnatin jihar Katsina za ta ƙirƙiro Wutar Lantarki a wasu asibitocin jihar Kwamishina lafiya na jihar Katsina yace a shirye-shiryen da Gwamna Raɗɗa yake don haɓɓaka kiwon lafiya a jihar, zai ƙirƙiro wutar lantarki domin bada wuta a wasu Asibitocin jihar Katsina nan da shekara mai zuwa. Kwashinan lafiya na jihar Katsina Dr. Bashir Gambo Saulawa shi ne ya bayyana haka a yayin kaddamar da kayayyakin gwaje-gwaje na cutar sida a Katsina wanda suka kaddamar tare da shugaban hukumar KATSACA Dr. Bala Nuhu Kankiya Sadaukin Kankia, a ranar Talata 19 ga watan Satumba 2023. Katsina Post ta samu cewa, daga cikin kayayyakin ayyuka a Asibitoci 347 dake faɗin jihar za a dauki wasu Asibitocin domin saka su cikin jerin waɗanda za a samar ma da wuta ta musamman don saka manyan kayan aikin da za a rinƙa gudanar da ayyukan kiwon lafiya ba sai an fita wata jiha ba. Kwashinan lafiyar yace Malam Dikko Umaru Raɗɗa yana nan a kan bakansa gameda samar da kayan ayyuka na zamani a ɓangaren kiwon lafiya a jihar Katsina, yace za su jajirce don ganin sun sauke nauyin da aka ba su a kowanne bangare a ma'aikatar kiwon lafiya.

Allah Ya Yi Ma Ɗanmasanin Kaita Rasuwa

Allah ya yi ma Ɗanmasanin Kaita rasuwa Ɗanmasanin Kaita, Malam Mustapha Dankama Allah ya yi ma sa rasuwa a Katsina Sheikh Mustapha Yusuf Dankama, wanda shi ne Ɗanmasanin Kaita Katsina Post ta samu rasuwar sa. An gudanar da jana'izarsa da misalin karfe 5:00 na yammacin Litinin 18 ga watan Satumba 2023 a gidansa dake Unguwar Taƙwiƙwi, Dankama a yankin ƙaramar hukumar Kaita dake jihar Katsina. Al'umma daban-daban ne sukai addu'a a gareshi a kan Allah ya yikansa da Rahama.

Yadda Farashin Abinci Yake Yau Litinin A Wasu Kasuwannin Jihar Katsina

Yadda farashin Abinci yake yau Litinin a wasu Kasuwannin jihar Katsina Kasuwar garin Dandume, ga yadda farashin sa yake kamar haka; 1- Buhun Masara fara - 54,000 ja sabuwa - 35,000 sabuwa - 32,000 2- Buhun Dawa - 47,000 3- Buhun Gero - 37,000 4- Buhun Dauro - 37,000 5- Buhun Dabino - 82,000 6- Buhun Wake - 65,000 ja - 62,000 sabo - 47,000 7- Buhun waken suya - 34,000 8- Buhun Aya - 50,000 kanana - 42,000 9- Buhun Gyada tsaba- 82,000 ja - 95,000 mai bawo - 22,000 10- Buhun Shinkafa tsaba - 73,000 shanshera - 31,000 ta tuwo - 82,000 11- Buhun Kalwa - 45,000 wankakka - 55,000 12- Buhun Dankali - 12,000 13- Buhun Tattasai solo - 6,000 kauda - 40,000 14- Buhun Albasa - 20,000 15- Buhun Kubewa busassa - 30,000 Kasuwar garin Dutsi , ga yadda farashin sa yake kamar haka; 1- Buhun Masara - 53,000 ja - 54,000 Sabuwa - 40,000 2- Buhun Dawa mori - 42,000 fara - 36,000 3- Buhun Gero - 40,000 4- Buhun maiwa - 40,000 5- Buhun Wake - 43,000 ja - 34,000 sabo - 41,000 6- Buhun Waken suya - 39,000 7- Buhun Shinkafa - 76,000 shanshera - 25,000 8- Buhun Gyada tsaba - 62,000 mai bawo - 27,000 9- Buhun Kalwa - 31,000 tsohuwa - 40,000 10- Buhun Alabo - 33,000 11- Buhun Aya kanana - 32,000 manya - 39,000 12- Buhun Dankali - 12,000 Kasuwar garin Mai'adua, ga yadda farashin sa yake kamar haka; 1- Buhun masara Sabuwa - 38,000 2- Buhun Dawa - 52,000 3- Buhun Gero - 33,000 4- Buhun Gyada - 67,000 Mai bawo - 25,000 5- Buhun Shinkafa tsaba - 65,000 shanshera - 32,000 6- Buhun Wake - 46,000 7- Buhun waken suya - 41,000 8- Buhun Alabo - 45,000 9- Buhun Tarugu ja - 17,000 10- Buhun Garin kwaki - 22,000 ja - 25,000 11- Buhun Dankali - 18,000 12- Buhun Makani - 13,000 Kasuwar garin 'Yantumaki a karamar hukumar Danmusa,ga yadda farashin sa yake kamar haka; 1- Buhun masara tsohuwa -40,000 Sabuwa - 34,000 2- Buhun Dawa - 36,000 3- Buhun Gero tsoho - 43,000 sabo - 40,000 4- Buhun Gyada tsaba - 77,000 mai bawo - 20,000 5- Buhun Shinkafa tsaba - 88,000 shanshera - 28,000 6- Buhun Wake - 52,000 sabo - 48,000 7- Buhun waken suya - 37,000 8- Buhun Alkama - 44,000 9- Buhun Kalwa - 28,000 10- Buhun Tattasai solo - 13,000 11- Buhun Tarugu solo - 20,000 12- Buhun Albasa - 18,000 13- Kwandon Tumatur - 10,000 Kasuwar garin Rimaye a karamar hukumar Kankiya,ga yadda farashin sa yake kamar haka; 1- Buhun Masara -50,000 sabuwa - 46,000 2- Buhun Dawa ja - 36,000 fara - 48,000 3- Buhun Gero sabo - 32,000 4- Buhun Dauro - 44,000 5- Buhun Kalwa - 24,000 6- Buhun Shinkafa - 84,000 Shanshera - 24,000 7- Buhun Gyada - 67,000 Mai bawo - 28,000 8- Buhun wake - 48,000 9- Buhun waken suya - 38,00 10- Buhun Barkono - 32,000 11- Buhun Dabino - 90,000 12- Buhun Dankali - 23,000 13- Buhun Tattasai - 55,000 14- Buhun Tarugu solo - 16,000 15- Kwando Tumatur kauda - 47,000 16- Buhun Dabino - 95,000 Kasuwar garin Charanci, ga yadda farashin sa yake kamar haka; 1- Buhun Masara - 50,000 Sabuwa 35,000 2- Buhun Dawa - 32,000 3- Buhun Gero - 46,000 4- Buhun Shinkafa - 67,000 5- Buhun Alabo - 40,000 6- Buhun Wake sabo - 46,000 tsoho - 50,000 7- Buhun Waken suya - 35,000 8- Buhun Tattasai - 15,000 9- Kwandon Tumatur - 4,000 10- Buhun Tarugu - 14,000 11- Buhun Albasa - 20,000 12- Buhun Dankali - 10,000 13- Buhun Alkama - 55,000 Daga Aysha Abubakar Danmusa

An Tsige Sarkin Kurayen Katsina, Hakimin Kuraye Daga Sarautar Shi

An tsige Sarkin Kuraye, Hakimin Kuraye daga sarautar shi Masarautar Katsina ta tsige Alhaji Abubakar Abdullahi Amadou daga sarautar shi ta Sarkin Kurayen Katsina, Hakimin Kuraye. Wannan na ƙunshe a cikin wata sanarwar da sakataren masarautar Katsina, Sarkin Yaƙin Katsina, Alhaji Bello Mamman Ifo ya sanya ma hannu. Sanarwar ta bayyana cewa Gwamnatin jihar Katsina ce ta bada umarnin tsige hakimin daga sarautar shi. Ga wasiƙar da masarautar ta aikewa hakimin: YI MAKA RITAYA DAGA SARAUTAR SARKIN KURAYEN KATSINA, HAKIMIN KURAYE: Bisa ga Takardar da Majalissa Mai-Martaba Sarkin Katsina Alh. (Dr.) Abdulmumini Kabir Usman CFR, ta samu daga Offishin Sakataren Gwamnati mai lamba KTS/SGS/SEC.54/T/7 ta ranar 15/9/2023, akan maganar Daura Auren Alh. Lawal Mamman Auta da Hajiya Halimatu Abdullahi Kuraye, wadda Gwamnatin Jiha ta bada umurnin Yi maka Ritaya daga Sarautar Sarkin Kurayen Katsina. Don haka, Masarautar Katsina ta yi maka Ritaya daga Sarautar Sarkin Kurayen Katsina daga Yau Litinin 18/9/2023. Da fatan Allah Ya bamu lafiya da zama lafiya amin.

Sa'in Katsina Ya Cika Shekaru 50 Cif A Sarautarsa

Sa'in Katsina Ya Cika Shekaru 50 Cif A Sarautarsa Maigirma Sa'in Katsina Amadu na Funtua ya cika shekaru 50 cif a sarautar Sa'in Katsina. Majiya mai tushe ta tabbatar da cewa a ranar 16 ga watan Satumba a shekarar 1973 ne aka naɗa Alhaji Amadu Na Funtua a matsayin Sa'in Katsina, inda jiya 16 ga watan Satumba 2023 ya cika shekaru 50 cif a bisa Sarautar Sa'in Katsina. Kamar yadda Katsina Post ta samu, Marigayi Sarkin Katsina Alhaji Dr. Usman Nagogo, shi ne wanda ya naɗa Alhaji Amadu na Funtua a shekarar 1973 a matsayin Sa'in Katsina. Sa'in Katsina Amadu na Funtua, a yanzu yana da shekaru 94 a duniya wanda yana daga chikin mutanen da suka yi tsawon rai cikin waɗanda aka baiwa sarauta a tun a wancen lokacin. Al'umma da yawa ne sukai Addu'ar a gareshi a kan Allah ya ƙara ma shi lafiya da nisan ƙwana.

A New Down At The Ministry Of Women Affairs- By Luqman Umar Kankia

A NEW DAWN AT THE MINISTRY OF WOMEN AFFAIRS. Appointing Haj Zainab M Musawa to lead the Ministry of Women Affairs was akin to putting a round peg in a round hole. In his campaign days, Governor Dikko Umar Radda made an unwavering pledge to integrate as many women as possible into his government aligning with the 35% Gender Affirmative Action mandated by the National Gender Policy in Nigeria (NGP). With three accomplished female Commissioners at the helm of affairs of key ministries, accompanied by a constellation of Special Advisers, Permanent Secretaries, Senior Special Assistants, and heads of various Departments, Agencies, and Parastatals, too numerous to mention here, one can rightly say the Governor has walked his talk. What adds value to this narrative is that these women are not just mere placeholders but, in the words of Governor Radda, 'Women with immense capacity.' In a strategic move that seems almost preordained, While Zainab Musawa takes her role as commissioner, her sister Hannatu was sworn in as a Minister. President Tinubu, renowned for his commitment to assembling the best brains into his cabinet, chose Hannatu Musawa to oversee the Ministry of Arts, Culture, and Creative Economy for Nigerians to tap into her vast knowledge and wealth of experience. The same could be said of her sister. Glancing at the rich resume of Zainab, from day one, I knew Governor Radda wouldn't let go of this vibrant, articulate, and versatile lady. Armed with a B.S.C. in Accounting from the prestigious University of Abuja, a master's in International Affairs and Strategic Studies from the Nigeria Defence Academy, as well as a master's in International Studies from the University of Liverpool, Musawa perfectly fits the qualities of people Governor Radda was looking for to populate his cabinet. As she entered the ministry, the new Commissioner was met with a warm welcome from the dedicated staff of the Ministry led by the indefatigable Permanent Secretary. That she found the Ministry in limbo was no exaggeration, and that she was starting from scratch was a stark reality she kept in mind. Without procrastination, she set the wheels in motion to turn the tides. Her first project was carrying out some renovations to make the Ministry's working environment more conducive for work. Next, she embarked on a statewide familiarization tour of the various agencies under the Ministry's umbrella. The sights she encountered were heartbreaking where she found structures in deplorable condition due to years of neglect. Presently, the Ministry is diligently collating data of all registered Women Affinity Groups (WAGs) and those who wish to register, with a view to having a robust and comprehensive database that will guide the Ministry in implementing its programs. The pace at which the Honorable Commissioner is moving bespeaks her passion, zeal, and profound commitment to rewriting the narratives. If this lady with an uncommon passion for women's development channels the same fervor that characterized her tenure at the Government Enterprise and Empowerment Program (GEEP), the women of Katsina State will have no reason to falter. The Ministry of Women Affairs has been reinvigorated. What was once a forgotten institution is now a bustling hive of activity. The Ministry's dedicated staff now conduct their duties with enthusiasm aware that there is a new sherrif in town. The future of Katsina State women more than ever holds a promise.

An Kama Wani Kasurgumin Dan Bindiga A Katsina

An kama wani kasurgumin dan bindiga a Katsina Rundunar Ƴan Sandan jihar Katsina ta kama wani ƙasurgumin ɗan ta'adda mai suna Saminu Usman ɗan asalin ƙaramar hukumar Jibia, wanda ake zargi da yin garkuwa da mutane. Wannan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da kakakin rundunar jihar Katsina ASP Abubakar Sadiq Aliyu ya fitar a madadin Kwamishinan ƴan sandan jihar. A cewar ASP Abubakar rundunar a ƙoƙarin ta na yaƙi da ƴan ta'adda da ta'addanci a jihar Katsina, ta samu nasarar cafke wani Saminu Usman mai shekaru 19 ɗan asalin ƙaramar Jibiya da ake zargi da aikata laifin yin garkuwa a ƙauyen tashar Hurera da ke cikin jibiya. ASP Abubakar Sadiq ya ƙara da cewa a ranar da akayi garkuwar, an kawo rahoton sace ɗan shekara 5 mai suna Usman Shu'aibu a ofishin ƴan sanda na Jibiya ta hanyar wani Shu'aibu Salisu ɗan asalin garin. A cewar sa, bayan ya tuntuɓi mahaifin yaron, ya buƙaci a biya shi Naira dubu 600,000.00 da wayar Android guda uku a matsayin kuɗin fansa, wanda uban ya biya ya amso ɗan sa. ASP Abubakar, ya bayyana cewa, bayan samun rahoton, jami'an rundunar suka bazama neman wanda ya aikata ta'addancin tare da gano shi a garin Lambata na jihar Naija. Kakakin rundunar yace a lokacin binciken, wanda ake zargin ya amsa aikata laifin tare da fadin cewar ya haɗa kai wajen ɗauke wani Rabe.

Jerin Yadda Farashin Abinci Yake Jiya Juma'a A Wasu Kasuwannin Jihar Katsina

Jerin yadda farashin Abinci yake Jiya Juma'a a wasu Kasuwannin jihar Katsina Kasuwar garin Dandume, ga yadda farashin sa yake kamar haka; 1- Buhun Masara fara - 54,000 ja -56,000 ja sabuwa- 36,000 sabuwa - 34,000 2- Buhun Dawa - 52,000 3- Buhun Gero - 36,000 4- Buhun Dauro - 56,000 5- Buhun Rogo - 32,000 6- Buhun Dabino - 90,000 7- Buhun Wake - 55,000 ja - 65,000 8- Buhun waken suya - 37,000 9- Buhun Aya - 52,000 kanana - 42,000 10- Buhun Gyada tsaba- 82,000 mai bawo - 21,000 11- Buhun Shinkafa tsaba - 86,000 shenshera - 36,000 ta tuwo - 80,000 12- Buhun Dankali - 18,000 13- Buhun Alkama - 51,000 14- Buhun Kalwa - 43,000 wankakka 55,000 15- Buhun Tattasai - 10,000 kauda - 40,000 16- Kwandon Tumatur - 5,000 kauda - 20,000 17- Buhun Tarugu - 15,000 solo - 7,000 18- Buhun Albasa - 20,000 19- Buhun Barkono - 35,000 Kasuwar garin Bindawa,ga yadda farashin sa yake kamar haka; 1- Buhun masara - 48,000 Sabuwa - 36,000 2- Buhun Dawa ja - 40,000 fara - 36,000 3- Buhun Gero - 30,000 4- Buhun Alabo - 28,000 5- Buhun Gyada tsaba - 65,000 mai bawo - 30,000 6- Buhun Shinkafa tsaba - 70,000 shanshera - 28,000 7- Buhun Wake kanana - 44,000 8- Buhun waken suya - 40,000 9- Buhun Tafarnuwa - 35,000 10- Buhun Dankali - 22,000 11- Buhun Tattasai Danye - 8,000 kauda- 47,000 12- Kwandon Tumatur - 2,500 13- Buhun Tarugu - solo - 14,000 14- Buhun Albasa - 25,000 15- Buhun Gishiri - 10,000 16- Buhun Citta - 35,000 17- Buhun Kanwa - 9,000 18- Buhun Barkono - 20,000 Kasuwar garin Dutsanma ,ga yadda farashin sa yake kamar haka; 1- Tiyar masara tsohuwa - 1,50 2- Tiyar Dawa - 900 3- Tiyar Gero - 800 sabo - 800 4- Tiyar Shinkafa - 2,100 5- Tiyar Gyada tsaba - 1,300 samfarera - 450 tsohuwa - 650 6- Tiyar waken suya - 1,100 7- Tiyar wake - 1,300 sabo - 1,300 8- Tiyar Alkama - 1,200 9- Tiyar Ridi - 2,100 10- Buhun Tattasai - 18,000 11- Buhun Tarugu Danye - 20,000 12- Kwandon Tumatur - 5,000 13- Damin Albasa - 1,000 14 Tiyar Barkono - 1,000 15- Buhun Dankali - 15,000 Makani - 18,000 Kasuwar garin Kankiya,ga yadda farashin sa yake kamar haka; 1- Buhun Masara - 36,000 2- Buhun Dawa - 40,000 3- Buhun Gero - 30,000 4- Buhun Gyada - 68,000 mai bawo - 22,000 5- Buhun Wake - 44,000 6- Buhun waken Suya - 40,000 7- Buhun Alkama - 56,000 8- Buhun Tattasai - 17,000 9- Kwandon Tumatur - 2,500 10- Buhun Tarugu - 15,000 11- Buhun Albasa - 20,000 Kasuwar garin Daura, ga yadda fara shin sa yake kamar haka; 1- Buhun Masara - 50,000 Sabuwa - 37,000 2- Buhun Gero sabo - 34,000 3- Buhun Dawa - 56,000 4- Buhun Alkama - 46,000 5- Buhun Gyada - 70,000 6- Shinkafa Tsaba - 75,000 _ 80,000 7- Buhun Wake fari Sabo - 39,000 ja sabo - 38,000 8- Buhun Waken Suya - 42,000 9- Kwandon Tumatur - 12,000 10- Buhun Tattasai solo - 12,000 11-Buhun Tarugu - 20,000 kore 20,000 12- Buhun Albasa - 25,000 Daga Aysha Abubakar Danmusa

Za A Kammala Aikin Titin Jirgin Ƙasan Da Ya Bi Ta Katsina Zuwa Maradi A Shekarar 2025

Za a kammala aikin titin Jirgin Ƙasan da ya bi ta Katsina zuwa Maradi a shekarar 2025 Ana ci gaba da shirye-shiryen kammala Aikin Titin jirgin kasan da ya taho daga Dawanau a jihar Kano zuwa Daura har cikin Katsina zuwa Maradi. Ministan sufurin, Alhaji Sa'idu Alƙali ya yi jawabin hakan ne a ranar Jumma'a, lokacin da ya jagoranci ziyarar duba aiki a ma'aikatar. A cewar sa duk abinda suka zo dubawa sun gani kuma bada jimawa ba za a kammala ayyukan cikin sauki da lumana ba tare da tsangwama ba tare da kuma ƙyayyade ayyukan 'yankwangilar. Kamar yadda Katsina Post ta samu, Ministan ya yi bayanin cewa an yi babban aiki wanda idan aka kammala shi zai dade ana amfanarsa bai lalace ba domin ayyukan akwai manufofi ma su kyau. Yace babbar kwangilar wadda take a ƙarƙashin jagoranci, Mr. Vadislav Bystreneko, ya ce yarjejeniyar da sukai da gwamnatin tarayya tun a shekarar 2021 ta kasance kimanin kuɗi dala biliyan 1.95 kuma sun sanya hannu kan ayyukan tare da alƙawarin kammalawa. Alhaji Sa'idu Alkali, ya ƙara da cewa tunda kafin a sake kudin ayyukan, sun ci gaba da wasu manyan ayyuka na zane-zanen, da binciken ƙasa, da kuma kulawa da ayyukan kwangilar. Daga ƙarshe Mr. Vladislav Byststeko yace gwamnatin tarayya ta kwantar da hankalinta gameda kammala aikin domin sun yanke shawara za su kammala ayyukan a shekarar 2025 domin aikin yana da matuƙar muhimmanci a yankunan Arewa. Idan baku manta ba, tsohon shugaban ƙasa Muhammadu Buhari shi ne ya bada aikin titin jirgin ƙasan tin lokacin shugabancin sa na shugaban kasar Najeriya.

Za'a Fara Tantance Daliban Da Za'a Ba Tallafin Karatu A Katsina⁩

Hukumar ba da tallafin karatu ta jihar Katsina ta ce za ta fara bayar da tallafin karatu ga dalibai yan asalin jihar Katsina da suka samu guraben a duk manyan makarantun jihar a ranar 18 ga watan Satumba. Kakakin hukumar Salisu Lawal Kerau ya bayyana haka ta cikin wata sanarwa da ya raba wa manema labarai a Katsina. Ya ce za a kammala biyan tallafin ne a ranar 9 ga watan Oktoba a manyan makarantu daban-daban na Katsina da kewaye. Don haka ana buƙatar duk sabbin ɗalibai su zo tare da kwafin takardar rajista, ko remitta, da ingantaccen katin shaida na makaranta, kafin karɓar shedar samun tallafin. Ya bayyana cewa da zarar an fara raba kudaden tallafin, za a fara ba tallafin ga ɗalibai yan asalin jihar Katsina dake a manyan makarantun jihar. Ya tabbatar da cewa daga baya hukumar za ta cigaba da bada tallafin ga sauran dalibai yan asalin jihar da ke karatu a dukkanin manyan makarantun ƙasar nan.

Jami'an Tsaro Sun Kama Wanda Ya Kashe Kwamandan 'yansanda A Yankin Dutsinma

Jami'an tsaro sun kama wanda ya kashe Kwamandan 'yansanda a yankin Dutsinma 'Yan sandan Katsina sun kama ɗaya daga cikin 'yanta'addan da a kwanakin baya suka kashe kwamandan yankunan ƙaramar hukumar Dutsinma, ACP Aminu Umar. Rundunar ‘yansanda a jihar Katsina ta ce ta kama wani ɗanbindiga mai shekaru 30, wanda ake zargin yana da hannu wajen kashe Kwamandan yankin Dutsinma, ACP Aminu Umar. Kamar yadda Katsina Post ta samu, jami'in hulɗa da jama'a na rundunar 'yansandan jihar Katsina ASP Abubakar Sadiq Aliyu shi ne ya bayyana haka a lokacin taron Manema Labarai a ranar Alhamis 14 ga watan Satumba 2023. Yace rundunar ‘yansandan da ke sintiri ta samu galaba a kan ‘yanbindigar ne a wani artabu da suka yi da ta kai ga rasa ransa da na wani jami’i wanda aka fi sani da Sabon Jini, an kama shi ne a ranar 30 ga watan Agusta. Wanda ake zargin ya fito ne daga Ƙauyen Tsaskiya da ke ƙaramar hukumar Safana a jihar Katsina. A cewar rundunar 'yansandan, wanda ake zargi ya kasance cikin jerin sunayen da rundunar 'yansandan ta ke nema ruwa a jallo bisa wasu laifuffuka, kamar satar mutane. Satar shanu da sauran munanan laifuka. ASP Abubakar Sadiq Aliyu yace wanda ake zargin an kama shi ne a lokacin da aka kama shi gameda da laifin yin garkuwa da wani Hussaini Nabara da ke Ƙauyen Kagara a ƙaramar hukumar Dutsinma, inda a nan ne ya tabbatar da faruwar lamarin a yayin zurfafa bincike aka gano shi danƙungiyar wani Abubakar ne mai suna Jankare, wanda fitaccen shugaban ‘yanfashi ne a yankin Dutsinma Tunda farko wanda ake zargin ya amsa laifin haɗa baki da wasu miyagun ‘yanbindiga domin yi wa marigayi ACP Umar kwanton ɓauna a yayin da rundunar ta kama mutum 35 a ranar 2 ga watan Satumba, a yayin da ake gudanar da bincike wanda ake zargin ya amsa laifin da ake zargin sa da shi. Idan ma su bibiyar labarai ba su manta ba, a ranar 5 ga watan Yuli ne ‘yanbindiga suka yi wa marigayi ACP Umar kwanton ɓauna suka kashe shi, yayin da yake jagorantar tawagar sintiri a aikin da suka saba yi na fatattakar ‘yanta’adda a yankin Dutsinma.